Filtrar por género
- 773 - Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabanbantaFri, 18 Sep 2026
- 772 - Ra'ayoyin masu sauraro kan ƴan aikin jarida dake fuskantar tarnaƙi a Afrika
Ƴancin aikin jarida na ci gaba da fuskantar tarnaƙi a wasu ƙasashen Afirka, saboda yayin da wasu ke fuskantar tursasawa a Najeriya, a Jamhuriyar Nijar kuwa ana tsare da Moussa Tchangari kusan shekaru biyu ba tare da shara’a ba, yayin da a hannu ɗaya, wani ɗanjaridar wato Moussa Kaka ya ɓata yau kwanaki 16 kenan.
A can kuwa Mali ko shekaran jiya litinin ma an yanke wa wani ɗanjaridar hukuncin ɗaurin shekaru biyu a gidan yari, kamar dai yadda ake cafkewa tare da tilasta ƴanjaridar da ra’ayoyinsu suka bambanta da na gwamnati, shiga aikin soji a Burkina Faso.
Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai yau.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Wed, 16 Sep 2026 - 771 - Ra'ayoyin masu sauraro kan hauhawar farashin man fetur a Najeriya
Hauhawar farashin man fetur na ci gaba da haifar da tarin matsaloli ga al’ummar Najeriya, inda a jihohi irinsu Sokoto, Kebbi da Zamfara, farashin lita ya doshi Naira dubu ɗaya da 500 a halin yanzu kuma kusan hakan farashin yake a mafi yawan jihohin arewacimn ƙasar.
Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai yau, musamman game da yadda ake samun hauhawar farashin akai-akai da kuma yadda wataƙila hakan ke shafar kasuwanci da kuma sufuri a yankunanku.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Tue, 15 Sep 2026 - 770 - Ranar yaƙi da jahilci ta duniya a bana ya duba yadda za a inganta ilimin manya
Ranar takwas ga watan Satumban kowacce shekara, rana ce da Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware, tun a shekarar 1960 a matsayin ranar yaƙi da jahilci, inda ake mayar da hankali wajen faɗakar da jama'ar a sassan duniya mahimmancin ilimi da samar da tsari ko dabarun koyar da mutanen da basu samu dama ba.
A mafi yawan ƙasashe dai an sha aiwatar da tsarin yaƙi da jahilci da ke bai wa dattijai ko masu manyan shekaru damar iya koyon rubutu da karatu a rayuwarsu.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
Tue, 08 Sep 2026 - 769 - Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabanbantaFri, 28 Aug 2026
- 768 - Ra'ayoyin masu sauraro kan kalaman tinzira jama'a da wasu ƴan siyasa suke
A Najeriya ana ci gaba da mayar da martani mai zafi sakamakon kalaman da shugaban ƙaramar hukumar Kuje da ke birnin Abuja Mista Samuel Shekwolo ya furta, kan cewa duk wanda baya goyon bayan jam’iyya mai mulki ta APC ya fice daga karamar hukumar.
Yayin da ake tunkarar zabe a Najeriya, sannu a hankali kalaman tunzuri da yiwa jama’a barazana a karuwa a tsakanin yan siyasa musamman daga bangaren jam’iyya mai mulki, ganin yadda a baya-bayan nan wani sanata daga jihar Osun ya umarci magoya bayan jam’iyyar da su kashe abokan hammaya a duk inda suka hadu.
Shin yaya kuke kallon hadarin irin waɗannan kalamai yayinda ake shirye-shiryen zabe a kasar?
Kuna ganin Najeriya zata iya daukar mataki kan masu aikata wannan katobara ganin yadda har yanzu ba’a kai ga hukunta wancan sanata ba?
Sai ku bayyana mana ra’ayoyinku kamar yadda aka saba.
Thu, 27 Aug 2026 - 767 - Ra'ayoyin masu sauraro kan sace masallata 600 a jihar Neja
A Najeriya al’umma na cike da zullumi a jihar Neja musamman bayan ƴan ta’adda sun saki wani bidiyo a kafafen sada zumunta wanda ke nuna mutane kusan 600, galibinsu mata da yara da kuma dattijai, waɗanda suka bayyana a matsayin masallatan da suka sace a gari na Borgu a Juma’ar da ta gabata.
Mahukunta sun ce suna ƙoƙarin ceto su, amma hankula ba su kwanta ba gannin an saba ruwa ƙasa na shanyewa.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Tue, 25 Aug 2026 - 765 - Ra'ayoyi kan yadda rashin bin ƙa'idojin gini ya haifar da ambaliya a Abuja da Kano
A Najeriya duk da gargaɗin da hukumar yanayi ta NIMET ta riƙa yi a lokuta da dama game da ambaliyar da wasu sassan ƙasar zasu fuskanta a damunar bana, wajen ganin an ɗauki matakan daƙile illar da hakan zai haifar.
Tuni aka ga wannan ambaliya a birane da dama ciki har da Abuja fadar gwamnatin ƙasar, birnin da ruwa ya shanye sassa da dama da ke matsayin ambaliya mafi muni da aka gani, wanda ake alaƙantawa da dalilai da dama ciki har da gine-gine kan magudanan ruwa, wannan na zuwa a dai dai lokacin da can a jihar Kano ma ake cike da fargabar makamanciyar ambaliyar....
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Tue, 18 Aug 2026 - 764 - Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda zaɓen gwamnan Osun ya gudana Najeriya
A Najeriya, Gwamna mai ci kuma ɗan takarar jam’iyar Accord Ademola Deleke ya lashe zaɓen jihar Osun da aka gudanar a ranar Asabar da ƙuri’u sama da dubu 511, yayin da ɗan takarar jam’iya APC mai mulkin ƙasar Bola Oyebamiji yazo na biyu da ƙuri’u dubu 444,815.
Kafin ranar zaɓen dai an fuskanci dambarwar siyasa da rikice-rikice da suka yi sanadin mutuwar mutane sama da 40.
Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabanbanta...
Mon, 17 Aug 2026 - 763 - Ra'ayoyin masu saurare kan yadda gwamnonin Najeriya suka yi buris da kudaden UBEC
A Najeriya, Hukumar Kula da Ilimin Firamare ta Kasa ta roƙi gwamnonin jihohi da su yi wa Allah su gaggauta karɓar sama da Naira biliyan 332 na kuɗaɗen tallafin daidaita tsarin ilimi.
Shugabar Hukumar Aisha Garba wanda ta yi wannan kira, ta ce bayaga Naira biliyan 65 da aka ware akwai kuma wasu Naira biliyan 267 da aka ware domin inganta makarantun firamare a ƙananan hukumomin faɗin ƙasar.
Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Oumarou Sanni.
Thu, 13 Aug 2026 - 762 - Ra'ayoyin masu sauraro kan yunƙurin haɗa kan ƴan adawa a Najeriya don fiida ɗan takara ɗaya
A Najeriya, ƙungiyar G –100 ta gamayyar wasu fitattun ƴan ƙasar kimanin 100 ta jagorancin wani sabon yunkurin ganin lallai sai jam’iyyun adawa sun yi haɗin guiwa domin fitar da ɗantakara ɗaya tilo da zai fafata da shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekara mai zuwa.
Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakken shirin tare da Oumar Sanni.
Wed, 12 Aug 2026 - 761 - Ra'ayoyin masu sauraro kan haramtawa yara amfani da kafafen sadarwa a wasu ƙasashe
Ana ci gaba da samun ƙarin ƙasashe a sassan Duniya da ke ɗaukar matakin taƙaitawa ko kuma haramta wa yara amfani da shafukan sada zumunta don basu kariya daga illolinsu.
A halin yanzu dai fiye da ƙasashe 20 ne ciki har da India, da China da Faransa da Ingila, suka ɗauki wannan mataki, tun bayan da Australia ta zama ƙasa ta farko da ta bayar da misalin hana yara ‘yan ƙasa da shekaru 16 shiga shafukan sada zumuntar.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Wed, 22 Jul 2026 - 760 - Ra'ayoyin masu sauraro kan lashe kofin duniya da Spain ta yi
Tawagar ƙasar Spain ta lashe gasar kofin duniya karo na biyu a tarihi, bayan ta doke Argentina da ke kare kambun a wasan ƙarshe da suka gudanar a daren jiya.
Ita kuma Ingila ta ƙare a matsayi na 3 ne inda ta lashe kyautar tagulla da ke zama kyauta ta farko da ta lashe a kofin duniya cikin shekaru 60, ya yin da Faransa ta ƙare a matsayi na 4.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Mon, 20 Jul 2026 - 759 - Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabanbantaFri, 17 Jul 2026
- 758 - Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwan mabanbantaFri, 10 Jul 2026
- 757 - Ra'ayoyin masu sauraro kan buƙatar majalisa na a dakatar da afuwa ga ƴan ta'adda
Majalisar dattijan Najeriya ta bukaci gwamnatin kasar da ta dakatar da shirin yin afuwa ko kuma sauya ɗabi’un tubabbun ƴan ta’adda a wani yunƙuri na dawo da su cikin al’umma, wanda ta ce ba ya taimakawa ƙoƙarin da ƙasar ke yi wajen yaƙi da ta’addancin da ya yi mata katutu.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Thu, 09 Jul 2026 - 756 - Ra'ayoyi kan ziyarar da wakilan Vatican suka kai wa Sarkin Musulmin Najeriya
Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Muhammadu Sa’ad Abubakar na uku, ya ce mutunta addinan juna, daina furta kalaman ƙiyayya ko tsatsauran ra’ayi, abubuwa ne da za su iya taimakawa ta fannin kyautata zamantakewa a tsakanin al’umma.
Wannan dai gargaɗi ne da ke ƙunshe a sanarwar da aka fitar bayan ganawar da aka yi a babban masallacin birnin Abuja tsakanin mai alfarma Sarkin Musulmin da kuma tawagar manyan jami’an Fadar Vatican ƙarƙashin jagorancin Archibishop Paul Richard Gallaghera.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Wed, 08 Jul 2026 - 755 - Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabanbantaFri, 03 Jul 2026
- 754 - Ra'ayoyin masu sauraro kan ambaliyar da ta afkawa ƙasashen gaɓar ruwan teku a Afrika
Birane da dama da ke gaɓar ruwan tekun ƙasashen Yammacin Afrika sun fuskanci ambaliyar ruwa wadda ta haddasa asarar rayuka da kuma salwatar dukiyoyi masu tarin yawa.
Birnin Accra na ƙasar Ghana da Abidjan Ivory Coast, a can ne aka samu asarar rayuka, yayin ambaliyar ta haddasa ɓarna ga gidaje da kadarori a biranen Lagos, Cotonou, Lome da sauransu.
Lura da abin da ya faru a waɗannan birane da kuma yadda damina ke ci gaba da sauka, shin ko akwai waɗansu matakai da ku ke saboda kasancewa a cikin shirin ko-ta-kwana?
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Thu, 02 Jul 2026 - 753 - Ra'ayoyin masu sauraro kan ci gaba da zanga-zangar ƙyamar baƙi a Afrika ta Kudu
Bayan cikar wa’adin ranar 30 ga watan jiya da suka bai wa ƴan-ci rani don ficewa daga ƙasar, daga ƙarshe dai masu adawa da zaman baƙi a Afirka ta Kudu sun ƙaddamar da zanga-zangar neman ala dole sai sun fice daga ƙasar.
Masu tarzomar dai na kallon ƴan asalin ƙasashen ƙetare a matsayin waɗanda suka mamaye gurabobin aiki, lamarin da ya jefe ɗimbin Ƴan Afirka ta Kudu cikin yanayin zaman kashe wando.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Wed, 01 Jul 2026 - 752 - Ra'ayoyin masu sauraro kan tsadar mai duk da faɗuwar farashinsa a duniya
Duk da cewa an samu faɗuwar farashin ɗanyan man fetur a kasuwar duniya sakamakon sulhun tsakanin Amurka da Iran, amma har yanzu ana ci gaba da fama da tsadar wannan makamashi a mafi yawan ƙasashen duniya.
A Najeriya tuni Hukumar kare masu amfani da kayan masarufi ta ƙasar ta yi gargaɗin cewa ko dai dillalan mai su karya farashi ko kuma ta ɗauki matakan ladaftarwa a kansu.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Tue, 30 Jun 2026 - 751 - Ra'ayoyin masu sauraro kan rawar ƙasashen Afrika a Gasar Kofin Duniya
Ƙasashen Afrika 9 daga cikin 10 da ke halartar gasar cin kofin duniya ne suka samu nasarar tsallakawa zuwa zagayen ƙasashen 32 na wannan gasa da ke gudana a ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico.
Wannan dai shi ke matsayin babban tagomashi da nahiyar ta Afrika ta taɓa samu a irin wannan gasa ta cin kofin duniya.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Mon, 29 Jun 2026 - 750 - Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabanbantaFri, 26 Jun 2026
- 749 - Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda matsalar tsaro ke kawo tarnaƙi ga manoma
Yayin da damina ta fara kankama a Tarayyar Najeriya, wani abu da ake fargaba shi ne yadda matsalar tsaro ke iya haddasa tarnaki ga aikin gona hatta ma a wannan shekara.
Kusan a kowace rana za a samu labarin cewa an kai hare-hare kan manoma da kan yi sanadiyyar kisa, yin garkuwa domin neman kuɗin fansa, yayin da a wasu lokuta ake tilasta wa manoman biyan haraji kafin ba su damar shiga gonakinsu.
Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Wed, 24 Jun 2026
Podcasts similares a Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
El Partidazo de COPE COPE
Herrera en COPE COPE
La Linterna COPE
Es la Mañana de Federico esRadio
La noche de Cuesta esRadio
Hondelatte Raconte Europe 1
Au Coeur du Crime Europe1
Affaires sensibles France Inter
LEGEND Guillaume Pley
El colegio invisible OndaCero
La Rosa de los Vientos OndaCero
Les grands dossiers de l'Histoire par Franck Ferrand Radio Classique
Espacio en blanco Radio Nacional
Enquêtes criminelles RTL
Entrez dans l'Histoire RTL
Le grand récit RTL
Les Grosses Têtes RTL
Les histoires incroyables de Pierre Bellemare RTL
L'Heure Du Crime RTL
El Larguero SER Podcast
SER Historia SER Podcast
Todo Concostrina SER Podcast
Un Libro Una Hora SER Podcast
HISTORIAS DE LA HISTORIA VIVA RADIO
